DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mutane miliyan 24 ne ke fama da karancin gani a Nijeriya – Binciken jami’ar Ebonyi

-

Shugaban Jami’ar tarayya ta David Umahi, Uburu (DUFUHS), dake jihar Ebonyi, Farfesa Jesse Uneke, ya bayyana cewa akalla ‘yan Najeriya miliyan 24 ne ke fama da matsalar rashin gani.

Rahoton jaridar Punch ya ruwaito farfesan ya bayyana hakan ne a lokacin wata tattaunawa da manema labarai kan ayyukan Cibiyar Idanu ta zamani da kuma Institute for Eye Health, Visual Sciences Research na jami’ar, a Uburu, karamar hukumar Ohaozara, jihar Ebonyi.

Google search engine

Ya ce, binciken da aka gudanar ta Nigeria National Blindness and Visual Impairment Survey ya nuna cewa sama da kashi 4.2% na ‘yan Najeriya masu shekaru 40 da haihuwa sama sun makance.

Haka kuma, kimanin mutane miliyan 4.25 da ke da shekaru 40 zuwa sama suna fama da matsakaiciyar nakasa ko tsananin matsalar gani.

Ya jaddada bukatar mutane su rika yin gwajin ido akai-akai, wayar da kai ga al’umma, tare da samar da magani mai saukin samu da kuma farashi mai rahusa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara