Mataimakin babban sufeton ‘yan sandan Najeriya shiyya ta 17 wanda ya hada da jihohin Ondo da Ekiti Mr. Ajani Omolabi, ya ce a halin yanzu jami’ai na da kyakkyawar alaka tare da saukin kai ga’ yan Najeriya.
Yayin tattaunawa da kamfanin dillancin labaran Najeriya NAN a Akure, Omolabi ya ce wannan ya biyo bayan tsarin gabatar da aikin dan sanda a zamanance, wanda ya ce yana taimakawa matuka wajen yaki da ayyukan laifi musamman a shiyyar.
Ya ce tsarin na bai wa jami’ai damar samun bayanai daga al’umma, tare da samun cikakkiyar fahimtar juna, kamar yadda jaridar punch ta ruwaito.
Kazalika ya ce an bayar da jerin lakcoci da tarukan kara wa juna sani domin inganta ayyukan jami’an ‘yan sanda a fadin Najeriya.



