DCL Hausa Radio
Kaitsaye

PDP na ƙoƙarin fitar da dan takarar shugaban ƙasa a 2027 – Okechukwu Osuoha

-

Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa ‘yan siyasa da dama suna shirin neman tikitin shugaban ƙasa a 2027, kuma ba wai fitattun mutanen da aka sansu ba.

Da yake hira da manema labarai mataimakin mai ba da shawara kan harkokin shari’a na PDP na ƙasa Okechukwu Osuoha, ya faɗa wa manema labarai cewa jam’iyyar ta na gudanar da tattaunawa da shawarwari a ɓoye domin gano wanda zai iya zama ɗan takara mai karɓuwa a fadin ƙasar.

Google search engine

Ya ce, mutane kamar tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan, tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na LP Peter Obi, da gwamnan Oyo, Seyi Makinde kadan ne daga cikin mutanen da ke aiki a bayan fage.

Ya kara da cewa yanzu abinda yafi muhimmanci a PDP shi ne tattaunawa da shawarwari da zummar neman ɗan takara da zai iya haɗa kan al’umma da samun goyon bayan ‘yan Nijeriya baki ɗaya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar shugaban kasa ta mayar wa Atiku martani cewa babu yunwa a Niijeriya

Fadar shugaban kasa ta ce gwamnatin Bola Ahmed Tinubu na tafiya kan madaidaiciyar hanya, tana mai musanta ikirarin tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, da...

Kotu ta daure wani dan Nijeriya a Amurka kan laifin zambar kudin gado

Wata kotu a Amurka ta yanke wa wani ɗan Najeriya mai suna Ehis Lawrence Akhimie hukuncin daurin shekaru fiye da takwas bayan an same shi...

Mafi Shahara