DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sarki Sanusi ya gargadi gwamnatin tarayya kan yawan ciyo bashi

-

Sarkin Kano na 15, kuma tsohon gwamnan babban bankin Nijeriya CBN Muhammadu Sanusi II, ya nuna damuwa kan yadda gwamnatin tarayya ke ci gaba da ciyo bashi ba tare da tsari ba.

Sarki Sanus ya yi wannan bayani ne a bikin Kano International Poetry Festival KAPFEST a Kano, inda ya ce bashin da ake bin Nijeriya ya kai Naira tiriliyan 150 a farkon shekarar 2025 zai iya jefa ƙasar cikin mummunar matsalar kuɗi nan da shekaru 20.

Google search engine

Sarki Sanusi ya yi gargadi cewa idan ba a yi amfani da wadannan makudan kudade wajen inganta ilimi da ƙarfafa matasa ba, abin ba zai yi wa kasar kyau ba.

Ya kuma ce maimakon duk waɗannan basussukan a yi amfani da su ne wajen koyar da matasa domin su ne za su biya shi, amma abin takaici ana cin bashin ba tare da saka hannun jari ba.

Sai dai ya yaba wa matakin cire tallafin man fetur, yana mai cewa hakan ya ceci ƙasar daga fadawa matsalar tattalin arziki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Bai kamata NAHCON ta fara shirin hajjin 2026 ba tare da ta bayar da bayanin kudaden da aka kashe a hajjin 2025 ba‘

Ƙungiyar Shugabannin Hukumomin Jin Dadin Alhazai ta Jihohin Nijeriya ta bukaci hukumar kula da aikin hajji ta Nijeriya (NAHCON) da ta gaggauta kammala daidaita bayanan...

Farfesoshin Nijeriya na cikin jerin na nahiyar Afrika da ba su da albashi mai kyau

Bayanan da jaridar Punch ta tattaro sun ce malamin jami'a a Nijeriya da ya kai matakin farfesa na samun matsakaicin albashi na dala 366 (kimanin...

Mafi Shahara