DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu ya kuduri aniyar magance matsalar rashin aikin yi ga matasa – George Akume

-

Sakataren gwamnatin Najeriya George Akume ya baiyana cewa gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta yi himma wurin magance matsalar rashin aikin yi da inganta rayuwar ‘yan Nijeriya.

Akume, a lokacin da sabbin shugabannin kungiyar matasa ta Nijeriya NYC, ƙarƙashin jagorancin Kwamared Jethro Annum suka kai masa ziyara a Abuja ya jaddada cewa shugaban kasa ya ƙaddamar da manufofi da tsare-tsaren da za su rage radadin rayuwa tare da samar da damar ci gaba ga matasa.

Google search engine

Ya ce gwamnatin su ta na da kyakkyawar alaka da matasa kuma za su ci gaba da tallafawa matasa a dukkan harkoki, ciki har da samar da sakatariyar da ta dace da kayan aiki domin sauƙaƙa wa matasan wajen jagoranci da wayar da kan sauran matasa a fadin Nijeriya saboda su amfana da shirye -shiryen gwamnatin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Bai kamata NAHCON ta fara shirin hajjin 2026 ba tare da ta bayar da bayanin kudaden da aka kashe a hajjin 2025 ba‘

Ƙungiyar Shugabannin Hukumomin Jin Dadin Alhazai ta Jihohin Nijeriya ta bukaci hukumar kula da aikin hajji ta Nijeriya (NAHCON) da ta gaggauta kammala daidaita bayanan...

Farfesoshin Nijeriya na cikin jerin na nahiyar Afrika da ba su da albashi mai kyau

Bayanan da jaridar Punch ta tattaro sun ce malamin jami'a a Nijeriya da ya kai matakin farfesa na samun matsakaicin albashi na dala 366 (kimanin...

Mafi Shahara