Hukumar zaɓen Nijeriya INEC ta yi gargaɗi ga ‘yan Nijeriya da su yi watsi da wata sanarwa da ke nuna za ta dauki ma’aikata da ake yadawa a shafukan sada zumunta.
A wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X a ranar Laraba, INEC ta bayyana cewa wannan sanarwar ta bogi ce.
Sanarwar ta ce an gano cewa masu yaudarar na amfani da wani wani shafin yanar gizo inda suke amfani da damar domin shiga bayanan mutanen da suka shiga shafin.
Hukumar ta yi bayani cewa ba ta da irin wannan shafin kuma a halin yanzu ba ta gudanar da wani shirin ɗaukar ma’aikata.



