DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga sun yi ajalin wani mutum da suka sace bayan karbar kudin fansa a jihar Gombe

-

Rahotanni daga ƙauyen Galumji da ke ƙaramar hukumar Dukku a jihar Gombe, sun tabbatar da cewa wasu ‘yan bindiga sun halaka wani mutum mai suna Hammayidi duk da cewa danginsa sun biya su naira miliyan biyar 5, kudin fansa.

An sace Hammayidi daga gidansa cikin dare kimanin makonni uku da suka wuce, sai dai duk da biyan kudin, an gano gawarsa da ta fara ruɓewa a ƙarƙashin gada a dajin da ke tsakanin Dukku da Akko.

Google search engine

Daily Trust ta rawaito cewa wani ɗan’uwansa ya bayyana cewa an daure shi,daga bisani aka yanka sannan aka harbe shi.

Sun ce sun tara kudin fansar ne ta hanyar sayar da amfanin gona da kuma dabbobinsu a kasuwar Dukku.

Bayan satar Hammayidi, ‘yan bindigar sun sake kai farmaki gidaje biyu a yankin, inda suka sace shanu biyu, sannan daga baya suka yi ƙoƙarin sace wani makwabcinsa wanda ya tsere, amma matarsa tana hannunsu har zuwa wannan lokaci.

Har zuwa lokacin kammala wannan rahoton,an yi ƙoƙarin samun rundunar ‘yan sandan jihar Gombe amma ba a samu ba domin mai magana da yawunsu DSP Buhari Abdullahi, bai amsa kiran waya ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara