Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta dage sauraron shari’ar tsohon shugaban hukumar inshorar lafiya ta ƙasa (NHIA), Farfesa Usman Yusuf, zuwa ranakun 19 da 20 ga watan Nuwamba, domin cigaba da shari’a kan tuhumar da ake yi masa da cin hanci da rashawa.
Mai shari’a Chinyere Nwecheonwu ta ɗage zaman ne bayan kammala tambayoyin ga shaida na farko daga bangaren masu shigar da ƙara.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa tun da farko, shaidar wanda shi ne tsohon darakta a NHIA, Attahiru Ibrahim, ya amince cewa shi ne ya rubuta ƙorafi zuwa hukumar EFCC akan Yusuf a lokacin da yake shugabancin NHIA. Amma rashin lafiyar da ya samu ya sa ba a cigaba da shari’ar a jiya ba.
Hukumar EFCC ta gurfanar da Yusuf a kan tuhuma biyar da suka shafi: karkatar da kudade, amfanar da kansa ta hanyar amincewa da siyan mota, yayin da Farfesa Yusuf din ya ƙi amincewa da laifukan da ake tuhumar sa da su.



