Wani rahoton jaridar Punch ya bayyana yadda wasu Farfesoshi a Najeriya ke fama da matsalar tarin basuka a rayuwarsu ta yau da kullum, sakamakon rashin albashi mai kyau.
A cewar su, halin ko-in-kula da gwamnati ke nunawa a kan sha’aninsu, na kara jefa su da iyalansu cikin mawuyacin hali.
Wannan ya zo a daidai lokacin da shugaban kungiyar malaman jami’o’i ta Najeriya ASUU, Emmanuel Piwuna ya nuna damuwa da yadda ya ce gwamnati ta fifita kudaden da ake bai wa masu rike da mukaman siyasa fiye da wadanda ke a bangaren ilimi.



