DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Fursunoni 68 ne suka samu nasara a jarabawar NECO ta 2025 a jihar Kano

-

Hukumar kula da gidajen gyaran hali ta Nijeriya reshen jihar Kano, ta bayyana cewa fursunoni 68 sun samu nasara a jarabawar NECO ta shekarar 2025.

Mai magana da yawun hukumar a jihar, CSC Musbahu Lawan, ne ya tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a Kano a ranar Litinin.

Google search engine

Ya ce wannan nasara ta samu ne sakamakon ingantaccen tsarin koyarwa na cibiyar gidajen gyaran hali da kuma cikakken tallafin gwamnatin Jihar Kano.

A cewarsa, shirin ya nuna yadda ake aiwatar da dokar Correctional Service Act ta shekarar 2019, wacce ta bai wa fursunoni damar koyon karatu da sana’o’i a gidajen yari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara