DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar wakilai ta umurci Akanta Janar na Nijeriya ya fitar bayanan aiyukan kwangilar Niara tiriliyan 2.4 da aka amince 

-

Majalisar wakilan Nijeriya ta umurci Akanta Janar na kasa, Shamsudeen Ogunjimi, da ya gabatar da cikakkun bayanai kan yadda aka biya kuɗaɗen kwangila na sama da naira tiriliyan 2.4 da gwamnatin tarayya ta amince da su.

Wannan na zuwa ne bayan tabbacin da ofishin Akanta Janar ya bayar cewa gwamnati ta amince da biyan kuɗaɗen kwangilar domin aiwatar da manyan ayyuka a fadin ƙasar.

Google search engine

A cewar wata sanarwa da sakataren yada labarai na mataimakin kakakin majalisar, Chief Levinus Nwabughiogu, ya fitar a Abuja, majalisar ta jaddada bukatar tabbatar da sahihancin ayyukan da aka biya, tare da gargadin gujewa biyan kuɗi ga ayyukan da ba su da amfani ga ‘yan ƙasa.

Mataimakin kakakin Majalisar, Hon. Benjamin Kalu, wanda shi ne shugaban kwamitin da majalisar ta gudanar da wani zama da gwamnati da ‘yan kwangila a baya, ya ce an cimma matsaya bayan wata zanga-zanga da ‘yan kwangila suka yi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara