Shugaban hukumar tara haraji ta Najeriya Zacch Adedeji ya ce duk da karuwar da aka samu a kudaden shiga, gwamnatin tarayya ba za ta daina ciyo bashi ba.
Jaridar Punch ta ruwaito Adedeji na cewa ciyo bashi ba ya nuni da raunin gwamnati, sai dai ma hakan wata dabara ce ta bunkasa tattalin arziki.
A cewar sa, gwamnatin na ciyo bashi ne sakamakon hangen nesa, musamman wajen bunkasa zuba hannun jari na lokaci mai tsayi.



