DCL Hausa Radio
Kaitsaye

IGP Kayode ya kai karar wasu manyan jami’an ‘yan sanda kan zargin yin karya a shekarun haihuwa

-

Babban sufeton ‘yan sandan Najeriya Kayode Egbetokun ya shigar da karar wasu manyan jami’ai biyar, kan zargin yin karya a shekaru da nufin tsawaita wa’adin aikinsu.

Daily Trust ta ruwaito cewa Kayode ya shigar da karar ce gaban wata babbar kotu a Abuja, yana zargin jami’an da rage shekaru a takardun su na shaidar haihuwa.

Google search engine

Wadanda babban sufeton ya shigar da karar dai sun hada da mai mukamin AIG, sai CP guda biyu, da kuma DCP baya ga wani ACP, wanda ya ce dukkanin su masu murabus ne.

Sai dai wasu daga cikin wadanda ake kara sun musanta wannan zargi, inda mai shari’a Yusuf Halilu ya sanya ranar 25 ga watan Satumba domin gurfanar da su a kuma fara zaman shari’a.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara