DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Katsina ta nada sabbin sakatarorin masarautun Katsina da Daura

-

Waɗanda aka nada din su ne Isah Ali a matsayin Sakataren masarautar Katsina da Ibrahim Abubakar a matsayin ma’aji sai Muhammad Salisu Aliyu a matsayin mai binciken kudi na cikin gida na masarautar Katsina.

Kazalika, gwamnatin jihar ta amince da nadin Gazali Muhammad a matsayin Sakataren masarautar Daura, sai Musa Yahaya a matsayin Ma’aji da kuma Ado Aliyu a matsayin mai binciken kudi na cikin gida na masarautar Daura.

Google search engine

Bayanin hakan na kunshe a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun babban Sakataren ma’aikatar kula da kananan hukumomi ta jihar Katsina Malam Jamilu Yakubu da DCL Hausa ta samu kwafi.

Sanarwar ta ce hakan ya biyo bayan sanya dokar kula da masarautu ta jihar Katsina ta shekarar 2025.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An gudanar da addu’o’in neman tsari daga hare-haren ‘yan bindiga a jihar Neja

Mazauna yankin jihar Neja ta Arewa sun gudanar da addu’o’i na musamman a filin Idi da ke Kontagora, hedkwatar karamar hukumar Kontagora, domin neman taimakon...

‘Yan siyasa a Nijeriya sun fi maida hanakali kan siyasa maimakon magance matsalolin al’umma – Sarkin Onitsha

Sarkin Onitsha, Igwe Nnaemeka Achebe, ya caccaki ‘yan siyasa bisa mayar da hankali kan siyasa maimakon gudanar da mulki yadda ya kamata tun kafin zaben...

Mafi Shahara