DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sojoji Nijeriya sun yi ajalin ‘yan ta’adda da dama cikin mako guda – DHQ

-

Hedikwatar tsaron Najeriya ta bayyana cewa dakarun ta sun yi ajalin ƴan ta’adda da dama, sun kuma kama akalla mutum 120 tare da kubutar da mutane 41 da aka yi garkuwa da su a fadin ƙasar cikin mako guda.

Daraktan hulɗa da jama’a na rundunar sojojin Najeriya, Manjo Janar Markus Kangye, ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai a Abuja a ranar Alhamis.

Google search engine

Ya ce hare-haren da aka gudanar tsakanin 14 zuwa 22 ga Satumba sun shafi Arewa maso Gabas, Arewa maso Yamma, Arewa ta Tsakiya, Kudu maso Kudu da kuma Kudu maso Gabas.

Manjo Janar Kangye ya jinjinawa dakarun sojin kasar, bisa jajircewa da ƙwarewa da suke nunawa, tare da kira ga al’umma da su ci gaba da bai wa sojoji sahihan bayanai a kan lokaci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara