DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An zargi Ganduje da hannu a badakalar tashar tsandauri ta Kano

-

Rahoton binciken jaridar Premium Times ya zargi cewa ya gano tsohon gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje, ya yi amfani da kujerarsa wajen karkatar da mallakar tashar Dala Inland Dry Port daga hannun gwamnatin jihar Kano zuwa hannun iyalansa da abokan sa na siyasa a jihar.

A shekarar 2006 zamanin gwamnatin Ibrahim Shekarau, jihar Kano ta mallaki kaso 20 bis 100 a tashar, inda babban ɗan kasuwa Ahmad Rabiu ke riƙe kaso 80 bisa 100 na hanun jari, wanda aka ce Jihar ta yi alƙawarin samar da ababen more rayuwa a shafin ginin tashar, amma ba ta aiwatar ba.

Google search engine

Sai a shekarar 2020, Ganduje ya amince da biyan Naira biliyan 2.3 daga baitul malin jihar don yin wadannan gine-gine, duk da cewa a lokacin jihar ba ta da hannun jari a cikin kamfanin.

Binciken ya ce daga baya an ƙara kwangilar zuwa fiye da Naira bilyan 4, inda aka bai wa FRI Construction Company Ltd. aikin, wacce aka danganta da tsohon ministan sufuri Abubakar Bawuro.

An tsara tashar ta Kano ne a matsayin hanyar sauƙaƙa shigo da kaya da fitar da su, domin rage jinkiri, da kuma ƙarfafa cinikayya da ƙasashen makwabta masu fama da rashin tashoshin ruwa irin su Nijar, Chadi, da Kamaru.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara