Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ya jaddada cewa gwamnatin shugaba Tinubu ba za ta manta da ‘yan kasar da ke zaune a kasashen ketare ba.
Kashim Shettima ya bayyana haka ne yayin wani taro da wasu ‘yan Najeriya a kasar Amurka, daidai lokacin da ake gabatar da babban taron majalisar dinkin duniya karo na 80, kamar yadda jaridar punch ta ruwaito.
A cewar sa, gwamnatin za ta ci gaba da tafiya da su, a dukkanin irin matakai da tsare-tsaren da take bullo da su da nufin tabbatar da kimar Najeriya a idon duniya.



