DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jerry Gana ba shi da hurumin cewa Jonathan zai tsaya takara a 2027 – Jam’iyyar PDP

-

Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa tsohon ministan yada labaran Najeriya Farfesa Jerry Gana ba shi da hurumin cewa Goodluck Jonathan zai tsaya takarar shugabancin Nijeriya a zaben 2027.

 

Google search engine

Jaridar Punch ta ruwaito sakataren jam’iyyar na kasa Debo Ologunaba na bayyana cewa, PDP ba ta rasa nagartattun masu tsaya mata takara ba bayan Goodluck Jonathan.

 

Martanin jam’iyyar ya biyo bayan da Farfesa Jerry Gana, ya bayyana cewa tsohon shugaban Nijeriya Goodluck Jonathan zai tsaya takarar shugabancin kasar, kuma zai kayar da gwamnatin Tinubu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara