Babbar kotun tarayya dake Abuja ta dage zaman shari’ar da ake tuhumar dan gwagwarmaya a Najeriya Omoyole Sowore, sakamakon rashin gabatar da takardar tuhuma.
Kotun karkashin jagorancin mai shari’a Muhammad Umar ta tsayar da ranar 27 ga watan Oktoba a matsayin ranar da za ta ci gaba da sauraron karar.
Hakan ya biyo bayan da lauyan Sowore, Marshal Abubakar ya ce ba a gabatar musu da takardar tuhuma ba, sannan ba a samu wakilci daga bangaren manhajar X da ke cikin shari’ar ba, kamar yadda Channels TV ya wallafa.
Hukumar tsaron farin kaya DSS ce dai ta maka Sowore, kamfanin Meta da kuma manhajar X kotu, kan wasu kalaman sukar gwamnatin shugaba Tinubu da dan gwagwarmayar ya wallafa a shafukansa na sada zumunta.



