DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta dage zaman shari’ar DSS da Sowore

-

Babbar kotun tarayya dake Abuja ta dage zaman shari’ar da ake tuhumar dan gwagwarmaya a Najeriya Omoyole Sowore, sakamakon rashin gabatar da takardar tuhuma.

Kotun karkashin jagorancin mai shari’a Muhammad Umar ta tsayar da ranar 27 ga watan Oktoba a matsayin ranar da za ta ci gaba da sauraron karar.

Google search engine

Hakan ya biyo bayan da lauyan Sowore, Marshal Abubakar ya ce ba a gabatar musu da takardar tuhuma ba, sannan ba a samu wakilci daga bangaren manhajar X da ke cikin shari’ar ba, kamar yadda Channels TV ya wallafa.

Hukumar tsaron farin kaya DSS ce dai ta maka Sowore, kamfanin Meta da kuma manhajar X kotu, kan wasu kalaman sukar gwamnatin shugaba Tinubu da dan gwagwarmayar ya wallafa a shafukansa na sada zumunta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara