DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sojojin Najeriya sun dakile harin ‘yan bindiga a jihar Benue

-

Sojojin Najeriya karkashin rundunar ‘Operation Whirl Stroke’ sun samu nasarar dakile wani hari da wasu ‘yan bindiga suka yi niyyar kai wa kan al’umma a karamar hukumar Katsina-Ala da ke jihar Benue.

Wata sanarwa da mukaddashin mai magana da yawun rundunar Laftanar Ahmad Zubairu ya fitar, ta bayyana cewa dakarun sojin sun dauki matakin hana kai harin ne a ranakun 26 da 28 ga watan Satumban 2025, kamar yadda jaridar punch ta ruwaito.

Google search engine

Sanarwar ta ce ‘yan bindigar sun yi niyyar kai hari ne a kauyukan Agurugu da Igyudu, inda dakarun sojin suka farmake su.

Baya ga dakile harin, sun kuma samu nasarar kwato miyagun makamai daga hannun su, bayan tarwatsa su da jami’an sojin suka yi, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara