DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Akwai gwamnoni daga jam’iyyun adawa da ke shirin komawa jam’iyyar APC – Sanata Godswill Akphabio

-

Shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana cewa wasu gwamnoni daga jam’iyyun adawa a Nijeriya na shirin komawa jam’iyyar APC domin goyon bayan shugabancin Bola Ahmed Tinubu.

A cewar wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Jackson Udom, ya fitar a Abuja, Akpabio ya yi wannan bayani ne a Owerri, jihar Imo, a yayin bikin ƙaddamar da littafin da Gwamna Hope Uzodimma ya rubuta tare da kaddamar da wasu ayyukan raya ƙasa da Shugaba Tinubu ya yi.

Google search engine

Ya ce saboda ayyukan da shugaba Tinubu ya yi a shekaru biyu da suka gabata, akwai gwamnoni da dama da suke jiran a karbesu cikin jam’iyyar APC.

Ya ƙara da cewa ‘yan Nijeriya sun fara jin daɗin sauye sauyen da gwamnatin Tinubu ta kawo, wanda suka taɓa rayuwar ɗalibai, manoma da ‘yan kasuwa a fadin kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dalung ya bukaci da a saki Abba Kyari cikin gaggawa

Kungiyar Movement for the Emancipation of Nigeria wato MEN, ta bukaci gwamnatin Nijeriya ta dakatar da shari’ar da ake yi wa tsohon mataimakin kwamishinan ‘yan...

Gwamnan Enugu ya fice daga jam’iyyar PDP zuwa APC

Gwamnan Jihar Enugu, Peter Mbah, ya sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC, inda ya bayyana cewa matakin nasa na da nufin kara inganta...

Mafi Shahara