DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babu yarjejeniyar da muka sa ma hannu kafin janye yajin aiki — PENGASSAN

-

Kungiyar manyan ma’aikatan man fetur da na gas (PENGASSAN) ta bayyana cewa babu wata yarjejeniya da suka sa wa hannu kafin janye yajin aikin da suka yi.

PENGASSAN ta janye yajin aikin ne a ranar Laraba bayan shiga da gwamnati ta yi tsakaninta da matatar man Dangote.

Google search engine

Da yake jawabi a wata hira da gidan talabijin na Channels, Shugaban Kungiyar, Featus Osifo ya bayyana cewa takardun da aka gabatar a zaman ba yarjejeniya ba ce don haka ba su rattaba hannu a kai ba saboda suna ganin akwai lauje cikin nadi.

Osifo ya kara jaddada matsayar kungiyar na dole Dangote ya mayar da ma’aikatan da aka dakatar aiki a wurarensu na asali sabanin sauya musu wajen aiki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara