Kungiyar likitoci ta Nijeriya ta koka kan yadda karancin likitoci da ke duba marasa lafiya inda ta siffanta hakan da saba ka’idar aikin.
A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar cikar Nijeriya shekaru 65 da samun ‘yancin kai, kungiyar ta sanar cewa, daga 1 ga watan Oktoba, likitoci a fadin kasar ba za su kara amsa kiran aikin da ya wuce awa 24 ba.
Sanarwar da ke dauke da sa hannun Shugaban kungiyar, Dr Mohammed Sulaiman, ta kara da cewa, Nijeriya na fama da karancin likitoci tare da yawaitar fitar su zuwa kasashen ketare domin neman albashi mai tsoka.



