DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Muna kira da kada Shugaba Tinubu ya saurari gwamnonin da ke son a kafa ‘yan sandan jihohi a Nijeriya – APC Forum

-

Kungiyar magoya bayan jam’iyyar APC ta Arewa ta Tsakiyar Nijeriya ta roƙi Shugaba Bola Tinubu da ‘yan majalisar dokoki ta ƙasa da kada su amince da buƙatun kafa rundunar ‘yan sanda ta jihohi a Najeriya.

Wannan kiran ya biyo bayan jawabin Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Mutfwang, wanda ya ce lokaci ya yi da za a samu ‘yan sandan jihohi domin magance matsalolin tsaro a jiharsa da sauran sassan ƙasar.

Google search engine

Sai dai a wata sanarwa da shugaban kungiyar, Alhaji Saleh Zazzaga, ya fitar a Abuja, kungiyar ta bayyana adawarta ga wannan shawara, tana mai cewa kafa ‘yan sandan jihohi zai zama barazana ga dimokuraɗiyya da zaman lafiya.

Kungiyar ta ce mafi yawan gwamnonin jihohi na amfani da karfin gwamnati wajen danniya da tsoratar da ‘yan adawa da ƙananan ƙabilu, don haka idan aka ba su cikakken iko da rundunar ‘yan sanda ta jihohi, za su yi barna fiye da yadda ake gani a yanzu.

Kungiyar ta ce musamman a yankin Arewa ta Tsakiya, inda ake da ƙabilu da addinai daban-daban, kafa ‘yan sandan jihohi zai iya haifar da rigingimu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara