DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Muna neman dauki kan yawan harin da dorinar ruwa ke kawo mana – Dan majalisar tarayya a Gombe

-

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Yamaltu/Deba a Jihar Gombe, Inuwa Garba, ya roki gwamnatin tarayya su kawo musu dauki kan hare-haren dorinar ruwa da suka addabi mazauna yankinsa.

Garba ya gabatar da wannan bukata ne a zaman da mataimakin kakakin majalisar wakilai Benjamin Kalu ya jagoranta, inda ya bayyana cewa hare-haren sun yi sanadin rasa rayukan wasu mafarauta da manoma a bakin koguna da gonaki.

Google search engine

Ya kara da cewa, hare-haren da ke faruwa a yankin sun haifar da tsoro da tashin hankali, abin da ya tilasta wasu manoma da masu kamun kifi barin aikinsu, lamarin kuma na kara ta’azzara talauci da rashin abinci.

A ranar 5 ga watan Oktoba, wata dorinar ruwa ta afkawa masunta a cikin kwale-kwale, inda ta kashe mutum daya mai suna Yahaya Bawa, ta kuma jikkata wasu da dama kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An gudanar da addu’o’in neman tsari daga hare-haren ‘yan bindiga a jihar Neja

Mazauna yankin jihar Neja ta Arewa sun gudanar da addu’o’i na musamman a filin Idi da ke Kontagora, hedkwatar karamar hukumar Kontagora, domin neman taimakon...

‘Yan siyasa a Nijeriya sun fi maida hanakali kan siyasa maimakon magance matsalolin al’umma – Sarkin Onitsha

Sarkin Onitsha, Igwe Nnaemeka Achebe, ya caccaki ‘yan siyasa bisa mayar da hankali kan siyasa maimakon gudanar da mulki yadda ya kamata tun kafin zaben...

Mafi Shahara