DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dan takarar majalisar dokoki na jam’iyyar PDP a jihar Zamfara ya sauya sheka zuwa APC

-

Dan takarar jam’iyyar PDP a zaben cike gurbi na majalisar dokokin jihar Zamfara na Kaura Namoda South, Muhammad Kurya, ya sauya sheka zuwa jam’iyyar APC.

Kurya ya sanar da sauya shekar tasa ne a Asabar dinnan yayin wani taro da aka gudanar a birnin Gusau na jihar Zamfara.

Google search engine

Jaridar Punch ta rawaito cewa wannan sauyin sheka ya biyo bayan zaben cike gurbi da hukumar INEC ta ayyana Kamilu Sa’idu na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben.

A cikin wata sanarwa da Kurya ya wallafa, ya zargi gwamnati da rashin magance matsalar tsaro lamarin da ya ce shi ne ya taimaka wajen faduwar sa zabe da kuma tabarbarewar tsaro a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Nijar ta kaddamar da sabon ofishin kamfanin shinkafar gida

Ministan kasuwancin jamhuriyar Nijar, Malam Abdoulaye Seydou ya jagoranci kaddamar da sabon ofishin kamfanin shinkafar gida a babban birnin Yamai a ranar Litinin 13 ga...

Gwamnatin Nijeriya za ta dauki mataki kan barnar kudaden shiga a bangaren hakar ma’adanai

Ministan ma’adanai, Dele Alake, ya bayyana cewa gwamnatin Nijeriya na shirin kafa sabuwar hukuma da za ta rika sa ido kan fitar da ma’adanai kafin...

Mafi Shahara