Mai horas da ƙungiyar Super Eagles ta Nijeriya, Eric Chelle, ya bayyana cewa ‘yan wasansa sun yi wasa da Lesotho cikin matsin lamba mai tsanani, duk da nasarar da suka samu da ci 2-1 a wasan cancantar shiga gasar cin kofin duniya ta 2026.
Chelle ya bayyana haka ne a taron manema labarai bayan tashi daga wasan a kasar ta Lethoto.
Ya ce tun a watannin da suka gabata,suke shan matsin lamba akan cin wasannin da za su bai wa Nijeriya damar zuwa gasar cin kofin duniya”World Cup”,duk da nasarar da suka samu amma akwai babban kalubale a gabansu dole su rubanya kokarinsu.



