DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Matsin rayuwar da ake ciki na shafar lafiyar kwakwalwar ‘yan Nijeriya, in ji Peter Obi

-

Tsohon dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party a zaben 2023, Peter Obi, ya bayyana cewa matsin rayuwa da ake fama da shi a yanzu ya fara shafar lafiyar kwakwalwar ‘yan Nijeriya.

Obi, ya bayyana haka ne a shafinsa na X yayin bikin ranar ranar lafiyar kwakwalwa ta duniya a ranar 10 ga Oktoba.

Google search engine

Ya ce talauci, rashin aikin yi da tsadar rayuwa sun sanya wasu matasa shiga cikin damuwa da aikata laifuka.

A cewarsa, rahoton hukumar lafiya ta duniya WHO ya nuna cewa sama da mutane miliyan 40 a Nijeriya na fama da matsalolin lafiyar kwakwalwa, amma ƙasa da likitocin kwakwalwa 300 ne kawai ke kula da su,wannan na nuna yadda ƙasar ke nuna halin ko in kula da fannin lafiya.

Obi ya bukaci gwamnati da ta ɗauki mataki kan wannan batun na kiwon lafiya, tare da buƙatar ƙara yawan likitocin kwakwalwa da kuma samar da asibitocin kwakwalwa a kowane yanki na ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara