DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Matsin rayuwar da ake ciki na shafar lafiyar kwakwalwar ‘yan Nijeriya, in ji Peter Obi

-

Tsohon dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party a zaben 2023, Peter Obi, ya bayyana cewa matsin rayuwa da ake fama da shi a yanzu ya fara shafar lafiyar kwakwalwar ‘yan Nijeriya.

Obi, ya bayyana haka ne a shafinsa na X yayin bikin ranar ranar lafiyar kwakwalwa ta duniya a ranar 10 ga Oktoba.

Google search engine

Ya ce talauci, rashin aikin yi da tsadar rayuwa sun sanya wasu matasa shiga cikin damuwa da aikata laifuka.

A cewarsa, rahoton hukumar lafiya ta duniya WHO ya nuna cewa sama da mutane miliyan 40 a Nijeriya na fama da matsalolin lafiyar kwakwalwa, amma ƙasa da likitocin kwakwalwa 300 ne kawai ke kula da su,wannan na nuna yadda ƙasar ke nuna halin ko in kula da fannin lafiya.

Obi ya bukaci gwamnati da ta ɗauki mataki kan wannan batun na kiwon lafiya, tare da buƙatar ƙara yawan likitocin kwakwalwa da kuma samar da asibitocin kwakwalwa a kowane yanki na ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Manyan Jami’an soji za su fuskanci ritayar dole bayan sauye-sauye a fannin tsaron Nijeriya

Rahotanni sun tabbatar da cewa akwai manyan jami'an sojin Nijeriya  masu mukamin Janar akalla 60 da za su fuskanci ritayar dole, biyo bayan sauye-sauyen da...

Rashin gogewar siyasa ta sa ban tsayar da El-Rufa’i don ya gaje ni ba – Obasanjo

Tsohon shugaban Nijeriya Olusegun Obasanjo ya bayyana cewa ya ki tsayar da tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasiru Elrufa'i don ya gaje a shekarar 2007...

Mafi Shahara