DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ministan Tinubu na ci gaba da samun sauki daga rashin lafiyar da ya kamu da ita in ji fadar shugaban kasa

-

Ministan Kudi kuma mai kula da harkokin tattalin arzikin ƙasa, Mr Wale Edun, yana jinya a gidansa da ke Abuja bayan ya kamu da rashin lafiya, kamar yadda majiyoyi daga fadar shugaban ƙasa suka tabbatar wa jaridar Punch a ranar Lahadi.

Wani babban jami’i a fadar shugaban ƙasa da ya nemi a sakaya sunansa ya bayyana cewa labarin da ke yawo cewa ministan ya kamu da shanyewar baren jiki ko kuma an kai shi ƙasashen waje don jinya ba gaskiya ba ne.

Google search engine

A cewarsa, “Eh, gaskiya yana rashin lafiya, amma ba shanyewar baren jiki ba ne. Yanzu haka yana cikin gidansa, ba a kai shi ko’ina ba.”

Majiyoyin sun kuma tabbatar cewa babu wani shiri daga Shugaba Bola Ahmed Tinubu na maye gurbin Mr Edun, yayin da ake sa ran lafiyarsa za ta inganta nan ba da jimawa ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara