DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Nada Amupitan a matsayin shugaban hukumar zaben Nijeriya INEC ya raba kan ‘yan adawa gida biyu a cewar jaridar Punch

-

Nadin Farfesa Joash Amupitan SAN a matsayin sabon shugaban hukumar zaben Nijeriya INEC da Shugaba Bola Tinubu ya yi, ya haddasa cece kuce a tsakanin jam’iyyun adawa, inda wasu ke ganin hakan zai tsarikan yin zabe.

Shugaba Tinubu dai ya bayyana cewa ya zabi Amupitan, ɗan asalin jihar Kogi, ne bisa cancanta mutunci da kwarewa, bayan majalisar koli ta Ƙasa ta amince da nadin nasa a ranar Alhamis, wanda ya zo bayan karewar wa’adin Farfesa Mahmood Yakubu a watan Oktoba 2025.

Google search engine

Sai dai yayin da ake shirin tura sunan sabon shugaban INEC zuwa majalisar dattawa domin tantancewa, shugabannin jam’iyyun adawa sun rabu gida biyu wasu na ganin nadin yana bisa doka, yayin da wasu ke ganin zai iya haifar da koma bayan siyasa a zaben 2027.

Jaridar Punch ta rawaito cewa,Sakataren rikon kwarya na jam’iyyar Labour Party,Tony Akeni, ya ce babu wata hujja ta doka da za ta hana Tinubu nada Amupitan, amma ya yi gargadin cewa hakan na iya zama cikas ga sahihancin zabe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara