DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu zai je kasar Italy a ranar Lahadi

-

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu zai bar Abuja yau Lahadi, domin halartar taron shugabannin kasashe da gwamnatoci na Aqaba Process a birnin Rome na kasar Italiya, wanda zai mayar da hankali kan matsalar tsaro a yankin Yammacin Afirka.

Kamar yadda fadar shugaban kasa ta sanar, taron zai fara ne a ranar 14 ga Oktoba, inda zai tattaro shugabannin kasashe, manyan jami’an leken asiri da sojoji daga kasashen Afirka, da kuma wakilan kungiyoyin kasa da kasa da na sa-kai, domin tattauna kalubalen tsaro da ke kara ta’azzara a Yammacin Afirka.

Google search engine

Shugaban kasa zai tafi da tawagar gwamnati da ta hada da Ministar Harkokin Waje mai kula da bangaren kasa da kasa, Ambasada Bianca Odumegwu–Ojukwu, Ministan Tsaro, Mohammed Badaru Abubakar, Mai ba da shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu, da Daraktan Hukumar Leken Asiri ta Kasa (NIA), Ambasada Mohammed Mohammed, da wasu manyan jami’an gwamnati.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara