DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ango da amarya sun shiga hannun Hisbah kan aure ba bisa ka’ida ba a jihar Kano

-

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama wasu matasa biyar bisa zargin gudanar da aure ba tare da amincewar iyaye ba, ciki har da ango da amarya da mutane uku da suka tsaya a matsayin wakilai da shaidu.

Mataimakin kwamandan hukumar, Dr. Mujahideen Aminuddeen, ya ce matasan sun daura auren ne bisa sadaki na Naira Dubu 10 wanda bai kai mafi ƙarancin da Musulunci ya tanada ba, abin da ya sa hukumar ta fara bincike kan lamarin.

Google search engine

Mujahideen ya bayyana cewa, auren ya sabawa ka’idojin Musulunci da na doka, yana mai kira ga iyaye da su kula da harkokin ‘ya’yansu musamman a batun da ya shafi aure.

Lamarin ya faru ne kasa da mako guda bayan gwamnatin Kano ta ba hukumar Hisbah umarnin fara shirin auren gata ga masu bukata fiye da 2,000 a fadin jihar kamar yadda Punch ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara