DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya za ta dauki mataki kan barnar kudaden shiga a bangaren hakar ma’adanai

-

Ministan ma’adanai, Dele Alake, ya bayyana cewa gwamnatin Nijeriya na shirin kafa sabuwar hukuma da za ta rika sa ido kan fitar da ma’adanai kafin jigilar su zuwa kasashen waje domin dakile ɓarnar kudaden shiga da kuma ƙara habaka tattalin arzikin kasar.

Alake ya bayyana hakan ne yayin taron manema labarai an Abuja gabanin taron Nigeria Mining Week karo na 10 da za a gudanar daga ranar 13 zuwa 15 ga watan Oktoba, 2025.

Google search engine

Hakazalika, Alake ya ce wannan sabon tsari ne da ke cikin manufofin gwamnati na tabbatar da gaskiya da cike gibi a harkokin kudaden shiga na ma’adanai.

A cewarsa, matakin na daga cikin shirin tattalin arzikin Shugaba Bola Tinubu na ƙara samun kudaden shiga bayan na albarkatun mai, ƙarfafa da’a ta ɓangaren kudi, da kuma mayar da masana’antar hakar ma’adinai daya daga cikin ginshikan bunkasar tattalin arzikin Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara