DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya za ta dauki mataki kan barnar kudaden shiga a bangaren hakar ma’adanai

-

Ministan ma’adanai, Dele Alake, ya bayyana cewa gwamnatin Nijeriya na shirin kafa sabuwar hukuma da za ta rika sa ido kan fitar da ma’adanai kafin jigilar su zuwa kasashen waje domin dakile ɓarnar kudaden shiga da kuma ƙara habaka tattalin arzikin kasar.

Alake ya bayyana hakan ne yayin taron manema labarai an Abuja gabanin taron Nigeria Mining Week karo na 10 da za a gudanar daga ranar 13 zuwa 15 ga watan Oktoba, 2025.

Google search engine

Hakazalika, Alake ya ce wannan sabon tsari ne da ke cikin manufofin gwamnati na tabbatar da gaskiya da cike gibi a harkokin kudaden shiga na ma’adanai.

A cewarsa, matakin na daga cikin shirin tattalin arzikin Shugaba Bola Tinubu na ƙara samun kudaden shiga bayan na albarkatun mai, ƙarfafa da’a ta ɓangaren kudi, da kuma mayar da masana’antar hakar ma’adinai daya daga cikin ginshikan bunkasar tattalin arzikin Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Nijar ta kaddamar da sabon ofishin kamfanin shinkafar gida

Ministan kasuwancin jamhuriyar Nijar, Malam Abdoulaye Seydou ya jagoranci kaddamar da sabon ofishin kamfanin shinkafar gida a babban birnin Yamai a ranar Litinin 13 ga...

Madugun adawar siyasa a kasar Kamaru na samun nasara a wuraren da Paul Biya ke da karfi a zaben da ke gudana a kasar

Sakamakon da ya fara shigowa daga zaben shugaban kasa na Kamaru ya nuna cewa dan takarar adawa, Issa Tchiroma Bakary, na samun nasara a yankunan...

Mafi Shahara