DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Harin da magoya bayan Kano Pillars suka kai ma 3SC abin Allah-wadai ne – Shehu Sani

-

Tsohon Sanata a Nijeriya, Shehu Sani, ya yi Allah-wadai da rikicin da magoya bayan Kano Pillars suka tafka bayan wasan NPFL da Shooting Stars ta Ibadan a Kano, inda suka kai wa ‘yan wasa da alkalan wasa hari.

Lamarin ya faru ne bayan Shooting Stars ta zura kwallo a minti na 94, inda ya daidaita sakamakon wasan da ya kare 1–1.

Google search engine

Shehu Sani ya bayyana cewa harin abin kunya ne da ke nuna rashin tsaro da kuma sakaci wajen kula da magoya baya a filayen wasa, yana mai cewa hakan na hana jama’a zuwa kallon wasannin cikin gida.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa jami’an tsaro sun yi amfani da barkonon-tsohuwa wajen tarwatsa magoya bayan da suka mamaye fili bayan kammala wasan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara