DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Madugun adawar siyasa a kasar Kamaru na samun nasara a wuraren da Paul Biya ke da karfi a zaben da ke gudana a kasar

-

Sakamakon da ya fara shigowa daga zaben shugaban kasa na Kamaru ya nuna cewa dan takarar adawa, Issa Tchiroma Bakary, na samun nasara a yankunan da Shugaban Kamaru, Paul Biya ke da karfi a siyasance kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Shugaba Biya mai shekara 92 na fuskantar ‘yan takara tara, ciki har da tsoffin abokansa a gwamnati kamar Bello Bouba Maigari, tsohon ministan yawon bude ido, da kuma Bakary, wanda ya kasance ministan kwadago kafin ya sauka daga mukaminsa.

Google search engine

Biya ya kada kuri’arsa a wata makaranta a birnin Yaoundé, inda ya ki bayyana makomarsa sai bayan an sanar da sakamakon zaben a hukumance.

Rahotanni daga kwamitocin zabe na kananan hukumomi sun nuna cewa jam’iyyar Bakary, FSNC, tana samun nasara a wurare da dama kan jam’iyyar mulki ta CPDM, yayin da wasu majiyoyi suka tabbatar da cewa, Bakary na kan gaba a mazabu da dama a birnin Yaoundé.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Nijar ta kaddamar da sabon ofishin kamfanin shinkafar gida

Ministan kasuwancin jamhuriyar Nijar, Malam Abdoulaye Seydou ya jagoranci kaddamar da sabon ofishin kamfanin shinkafar gida a babban birnin Yamai a ranar Litinin 13 ga...

Gwamnatin Nijeriya za ta dauki mataki kan barnar kudaden shiga a bangaren hakar ma’adanai

Ministan ma’adanai, Dele Alake, ya bayyana cewa gwamnatin Nijeriya na shirin kafa sabuwar hukuma da za ta rika sa ido kan fitar da ma’adanai kafin...

Mafi Shahara