DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dalung ya bukaci da a saki Abba Kyari cikin gaggawa

-

Kungiyar Movement for the Emancipation of Nigeria wato MEN, ta bukaci gwamnatin Nijeriya ta dakatar da shari’ar da ake yi wa tsohon mataimakin kwamishinan ‘yan sanda, Abba Kyari, tare da sakin sa nan take.

A wata sanarwa da shugaban kungiyar, tsohon ministan wasanni, Solomon Dalung, ya fitar a ranar Talata, Dalung ya ce, ci-gaba da tsare Kyari babban rashin adalci ne ganin cewa an ba wasu da aka yanke wa hukunci afuwa ciki har da masu safarar miyagun kwayoyi da masu garkuwa da mutane da daga cikin su tawagar Kyari ce ta kama.

Google search engine

An gurfanar da Kyari da wasu mutane 6 a gaban kotu a watan Maris 2022 bisa zargin hada baki wajen safarar kilo 21.35 na hodar-iblis da hukumar NDLEA ta kama daga hannun masu safarar miyagun kwayoyi kamar yadda Punch ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara