DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Fitar Pantami daga APC ba karamar asara ba ce ga jam’iyyar a Arewacin Nijeriya

-

Jigo a jam’iyyar APC daga Jihar Bauchi, Khamis Darazo, ya bayyana cewa ficewar tsohon ministan sadarwa da tattalin arzikin zamani, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, daga jam’iyyar zai kasance babban rashi ga APC musamman a Arewacin Nijeriya.

Darazo ya bayyana haka ne a ranar Lahadi yayin da yake zantawa da manema labarai a Bauchi, inda ya bukaci fadar shugaban kasa da shugabancin jam’iyyar su gaggauta shawo kan lamarin.

Google search engine

A cewarsa, rahotannin da ke cewa Pantami na shirin barin jam’iyyar suna kara tada hankalin magoya baya, yana mai gargadin cewa hakan zai zama babban koma baya ga jam’iyyar a Arewa da ma kasa baki daya.

Punch ta ruwaito cewa, Darazo ya bayyana Pantami a matsayin mutum mai hangen nesa da kwarewa wanda ya sadaukar da kansa wajen yada ilimi, imani da gaskiya wajen inganta mulki da kuma karfafa matasa a fadin Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara