DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan Kaduna ya halarci zaman majalisar wakilai yayin da ‘yan majalisar PDP 3 daga Jihar suka koma APC

-

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya halarci zaman majalisar wakilan tarayya a ranar Talata domin shaida sauya shekar wasu ‘yan majalisar jam’iyyar PDP uku zuwa jam’iyyar APC.

Wadanda suka sauya sheka su ne Abdulkarim Hussain Mohammed, Aliyu Mustapha Abdullahi da Sadiq Ango Abdullahi, kamar yadda Kakakin majalisar, Abbas Tajudeen, ya sanar yayin zaman majalisar.

Google search engine

Kafin taron, majalisar ta dakatar da wasu ayyuka nata domin ba gwamnan damar halartar zaman, inda daga bisani ya jagoranci sabbin ‘yan jam’iyyar APC wajen gaisawa da kakakin majalisar da daukar hoto tare kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Sai dai jagoran ‘yan majalisar adawa, Kingsley Chinda, ya yi watsi da sauya shekar, inda ya bukaci kakakin majalisar da ya bayyana kujerunsu a matsayin babu mai rike da su bisa tanadin kundin tsarin mulki na kasa sashe na 68.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnonin da suka sha suka ta yanzu sun koma jam’iyyar APC – Ministan Abuja Wike

Ministan birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya ce ficewar wasu gwamnonin jam’iyyar adawa ta PDP zuwa jam’iyyar APC ta tabbatar da goyon bayansa ga Shugaba...

Majalisar Dattawan Nijeriya za ta tantance sabon shugaban INEC ranar Alhamis

Majalisar Dattawan Nijeriya ta shirya tantance Farfesa Joash Amupitan, wanda shugaba Bola Ahmed Tinubu ya zaba domin zama sabon shugaban hukumar zaben Nijeriya INEC, a...

Mafi Shahara