DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ni na roki gwamnati da ta yafe ma Maryam Sanda – Mahaifin Bilyaminu Bello

-

Mahaifin marigayi Bilyaminu Bello, Alhaji Ahmed Bello Isa, ya bayyana cewa ya karɓi afuwar da Shugaba Bola Tinubu ya bai wa surukarsa, Maryam Sanda, yana mai cewa tun da dadewa ya yafe mata bisa kisan ɗansa da ta yi.

A yayin taron manema labarai an Abuja, Alhaji Bello ya ce afuwar shugaba Tinubu “nufin Allah ce,” wacce za ta bai wa Maryam damar kula da ’ya’yanta biyu.

Google search engine

Haka kuma ya ce a matsayinsu na Musulmai, sun amince da duk abin da Allah Ya kaddara, yana mai jaddada cewa “ramuwar gayya ba za ta dawo da Biliyaminu ba, amma yafiya na kawo salama.”

Maryam Sanda, ’yar tsohuwar ma’aikaciyar Aso Savings, an yanke mata hukuncin kisa a watan Janairu 2020 bayan samun ta da laifin kisan mijinta, Bilyaminu Bello, ɗan uwan tsohon shugaban jam’iyyar PDP, Alhaji Bello Haliru Mohammed.

Lamarin da ya faru a watan Nuwamba 2017 an Abuja ya tayar da ƙura a fadin ƙasar kan matsalar tashin hankali tsakanin ma’aurata da batun adalci.

Alhaji Bello ya bayyana cewa tun kafin kotu ta yanke hukunci a 2019, ya riga ya roƙi gwamnati ta yi Maryam Sanda afuwa kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kashi 8 cikin 100 na ‘yan Nijeriya ne kawai ke iya wanke hannu yadda ya kamata a cewar UNICEF

Asusun tallafawa kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya ce kaso 92 cikin 100 na 'yan Nijeriya ba sa iya wanke hannu yadda ya...

Majalisar wakilan Nijeriya ta gayyaci Gwamnan babban bankin kasar CBN kan wasu cajin kudade da bankuna ke yi wa al’umma

Majalisar wakilan Nijeriya ta gayyaci Gwamnan babban bankin CBN, Olayemi Cardoso, tare da shugabannin manyan bankuna domin bayyana dalilin cajin kudade ba tare da daliliba...

Mafi Shahara