DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaban hukumar zabe na jihar Yobe ya rasu

-

Shugaban hukumar zabe na jihar Yobe, Dr. Muhammad Mamman, ya rasu bayan gajeriyar rashin lafiya a asibitin koyarwa na garin Damaturu.

Rahotannin da Daily Trust ta wallafa sun tabbatar da cewa, marigayin ya rasu bayan gajeriyar rashin lafiya, inda ya bar mata uku da ’ya’ya 33 da jikoki.

Google search engine

Wasu rahotanni daga jaridar Daily Trust sun bayyana cewa an yi jana’izarsa da safe a babban masallacin fadar Mai Martaba Sarkin Fika a Potiskum, Jihar Yobe, inda jama’a da dama suka halarta domin yi masa addu’o’i.

Dr. Mamman, wanda gogaggen likita ne ya taɓa jagorantar hukumar kula da asibitoci ta Jihar Yobe a lokacin mulkin tsohon Gwamna Ibrahim Geidam. Daga baya Gwamna Mai Mala Buni ya sake naɗa shi sau biyu a matsayin shugaban hukumar zabe ta jihar Yobe, kuma yana kan wa’adinsa na ƙarshe kafin rasuwarsa.

Marigayin ya riƙe matsayin babban likita na Masarautar Fika, daga bisani kuma aka ɗaukaka shi zuwa Shamakin Fika. Ya kasance mutum mai tawali’u, nagarta da kishin al’umma da fatan Allah Ya jikansa da rahama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara