DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar wakilan Nijeriya ta bukaci karin jami’an tsaro domin yaki da ‘yan bindiga a jihar Sokoto

-

Majalisar wakilan Nijeriya ta bukaci rundunar soji, ’yan sanda da sauran hukumomin tsaro su yi hadin gwiwa tare da aiki domin dakile yawaitar hare-haren ’yan bindiga a kananan hukumomin Kebbe da Tambuwal na Jihar Sokoto.

Bukatar ta biyo bayan kudurin da dan majalisa mai wakiltar Kebbe/Tambuwal, Hon. Abdussamad Dasuki, ya gabatar a zauren majalisa ranar Talata.

Google search engine

Dasuki ya nuna damuwa kan yadda rashin tsaro ke ta karuwa a yankin, inda ya ce hare hare da dama da suka faru tsakanin watan Yuli da Agusta 2025,an yi garkuwa da mutane tare da halaka mutane da dama da kuma raba al’ummomi da muhallansu.

Bisa wannan dalilin majalisar ta umarci hukumomin tsaro da su kara tura jami’ai da kuma hada kai wajen gudanar da aiki a yankunan da abin ya shafa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsare-tsaren Tinubu na farfaɗo da martabar Nijeriya a duniya -Kashim Shatima

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya ce gyare-gyaren da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke aiwatarwa na sake gina martabar Nijeriya a idon duniya tare...

Gwamnatin Nijeriya na shirin dakatar da shigo da kayan tsaro daga waje

Gwamnatin Nijeriya ta yi niyyar kera dukkan makami da ake buƙata a cikin gida nan da shekara biyu zuwa biyar masu zuwa. Minista a ma'aikatar Tsaron...

Mafi Shahara