DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar wakilan Nijeriya ta gayyaci Gwamnan babban bankin kasar CBN kan wasu cajin kudade da bankuna ke yi wa al’umma

-

Majalisar wakilan Nijeriya ta gayyaci Gwamnan babban bankin CBN, Olayemi Cardoso, tare da shugabannin manyan bankuna domin bayyana dalilin cajin kudade ba tare da daliliba daga asusun al’umma a fadin kasar.

Wannan mataki ya biyo bayan kudurin da dan majalisar mai wakiltar Ilorin West/Asa, Hon. Muktar Shagaya, ya gabatar a zaman majalisar ranar Talata, inda ya zargi bankuna da yin cajin kudade da yawa ba tare da dalili ba, wanda hakan ya saba da dokokin da CBN ta shimfiÉ—a.

Google search engine

Ya ce irin wannan dabi’a tana lalata amincewar jama’a ga bankuna da kuma taimakawa wajen hana jama’a rungumar ajiye kudade a bankuna.

Majalisar ta umarci kwamitin tsare-tsaren bankuna da ya gudanar da zaman bincike cikin makonni huÉ—u, tare da umartar Cardoso da shugabannin bankuna su bayyana yadda ake cire kudaden da kuma daukar mataki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnonin da suka sha suka ta yanzu sun koma jam’iyyar APC – Ministan Abuja Wike

Ministan birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya ce ficewar wasu gwamnonin jam’iyyar adawa ta PDP zuwa jam’iyyar APC ta tabbatar da goyon bayansa ga Shugaba...

Majalisar Dattawan Nijeriya za ta tantance sabon shugaban INEC ranar Alhamis

Majalisar Dattawan Nijeriya ta shirya tantance Farfesa Joash Amupitan, wanda shugaba Bola Ahmed Tinubu ya zaba domin zama sabon shugaban hukumar zaben Nijeriya INEC, a...

Mafi Shahara