DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar wakilan Nijeriya ta gayyaci Gwamnan babban bankin kasar CBN kan wasu cajin kudade da bankuna ke yi wa al’umma

-

Majalisar wakilan Nijeriya ta gayyaci Gwamnan babban bankin CBN, Olayemi Cardoso, tare da shugabannin manyan bankuna domin bayyana dalilin cajin kudade ba tare da daliliba daga asusun al’umma a fadin kasar.

Wannan mataki ya biyo bayan kudurin da dan majalisar mai wakiltar Ilorin West/Asa, Hon. Muktar Shagaya, ya gabatar a zaman majalisar ranar Talata, inda ya zargi bankuna da yin cajin kudade da yawa ba tare da dalili ba, wanda hakan ya saba da dokokin da CBN ta shimfiɗa.

Google search engine

Ya ce irin wannan dabi’a tana lalata amincewar jama’a ga bankuna da kuma taimakawa wajen hana jama’a rungumar ajiye kudade a bankuna.

Majalisar ta umarci kwamitin tsare-tsaren bankuna da ya gudanar da zaman bincike cikin makonni huɗu, tare da umartar Cardoso da shugabannin bankuna su bayyana yadda ake cire kudaden da kuma daukar mataki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara