DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar wakilan Nijeriya ta gayyaci Gwamnan babban bankin kasar CBN kan wasu cajin kudade da bankuna ke yi wa al’umma

-

Majalisar wakilan Nijeriya ta gayyaci Gwamnan babban bankin CBN, Olayemi Cardoso, tare da shugabannin manyan bankuna domin bayyana dalilin cajin kudade ba tare da daliliba daga asusun al’umma a fadin kasar.

Wannan mataki ya biyo bayan kudurin da dan majalisar mai wakiltar Ilorin West/Asa, Hon. Muktar Shagaya, ya gabatar a zaman majalisar ranar Talata, inda ya zargi bankuna da yin cajin kudade da yawa ba tare da dalili ba, wanda hakan ya saba da dokokin da CBN ta shimfiɗa.

Google search engine

Ya ce irin wannan dabi’a tana lalata amincewar jama’a ga bankuna da kuma taimakawa wajen hana jama’a rungumar ajiye kudade a bankuna.

Majalisar ta umarci kwamitin tsare-tsaren bankuna da ya gudanar da zaman bincike cikin makonni huɗu, tare da umartar Cardoso da shugabannin bankuna su bayyana yadda ake cire kudaden da kuma daukar mataki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

NNPP ta bukaci Fadar Shugaban Nijeriya ta wanke Kwankwaso daga zargin tallafa wa ta’addanci

Jam’iyyar NNPP reshen Kano ta bukaci Fadar Shugaban Nijeriya da Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro (NSA) su fito su wanke jagoranta na...

Kotu a Kano ta daure jarumar Kannywood Samha Inuwa watanni 6 a gidan gyaran hali

Alkalin Babbar Kotun Tarayya da ke Kano, Mai shari’a S.M. Shuaibu, ya yanke wa jarumar Kannywood, Saadatu Mohammed Inuwa wadda aka fi sani da Samha,...

Mafi Shahara