DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tattalin arzikin Nijeriya zai bunkasa da kashi 3.9 cikin ɗari a 2025 a cewar IMF

-

Asusun ba da lamuni na duniya IMF ya bayyana cewa tattalin arzikin Nijeriya zai bunkasa da kashi 3.9 cikin ɗari a shekarar 2025, wanda ya zarta hasashen da ta yi a baya da kashi 0.5 cikin ɗari.

A cewar rahoton IMF da aka gabatar a taron shekara-shekara na bankin Duniya da IMF a birnin Washington DC ranar Talata, an samu wannan hasashe ne saboda daidaituwar tattalin arziki, karuwar masu zuba jari, da kuma fitar da man fetur.

Google search engine

Rahoton ya nuna cewa a 2026 tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da karuwa zuwa kashi 4.2 cikin ɗari musamman yadda darajar Naira ta karu.

Bankin Duniya ma ya yi hasashen cewa tattalin arzikin Nijeriya zai samu ci gaba da kashi 4.4 cikin ɗari a 2027, wanda zai samu ne daga ɓangaren harkokin noma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar Dattawa ta tabbatar da Farfesa Amupitan a matsayin shugaban hukumar zaben Nijeriya INEC

Majalisar Dattawan Nijeriya ta tabbatar da nadin Farfesa Joash Amupitan a matsayin sabon shugaban hukumar zaben Nijeriya INEC. Jaridar Punch ta ruwaito cewa majalisar ta amince...

Sarkin Musulmi ya bukaci gwamnati da ta yi doka kan amfani da kafafen sada zumunta

Sarkin Musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar III ya bukaci gwamnati da ta yi doka domin daidaita amfani da kafafen sada zumunta a Nijeriya saboda yadda ake...

Mafi Shahara