DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnati Nijeriya tace haryanzu ba a saki kowa ba a cikin mutanen da Tinubu ya yiwa afuwa

-

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa har yanzu ba a saki wani daga cikin mutanen da shugaba Tinubu ya yi wa afuwa ba.

Babban lauyan gwamnati kuma Ministan shari’a, Lateef Fagbemi SAN, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Alhamis dinnan.

Google search engine

Ya ce duk da amincewar majalisar koli ta kasa ana cikin matakin ƙarshe na duba da tabbatar da sunayen waɗanda suka cancanci afuwa kafin fitar da takardun saki.

Fagbemi ya jaddada cewa babu wani jinkiri a cikin tsarin, illa dai gwamnati na bin doka da ka’idoji don tabbatar da gaskiya da adalci,ana bin tsarin doka ne don tabbatar da cewa duk wanda aka yi wa afuwa ya cancanta

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Manufofin tattalin arzikin Tinubu sun taimaka wajen samun dumbin arziki a Nijeriya – Hope Uzodimma

Gwamnan jihar Imo, Hope Uzodimma, ya ce manufofin tattalin arziƙin da shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bijiro dasu sun taimaka wajen farfaɗo da tattalin arziƙin...

Jami’ar kimiyya da fasaha ta Aliko Dangote da ke Wudil a Kano, ta kori dalibai 34 bayan an same su da laifin satar...

Jami’ar kimiyya da fasaha ta Aliko Dangote da ke Wudil a Kano, ta kori dalibai 34 bayan an same su da laifin satar amsa a...

Mafi Shahara