DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Kano ta yi karar Ganduje da ‘ya’yansa bisa zargin almundahanar Naira biliyan 4.49

-

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, da ‘ya’yansa biyu da wasu mutum shida kotu bisa zargin yin almundahanar kudi naira biliyan 4.49.

Gidan talabijin na Channels ya rawaito cewa an shigar da karar ne a babbar kotun jihar Kano a ranar 13 ga Oktoba, 2025, inda gwamnati ke neman a maido da kashi 20 cikin 100 na kudaden da aka zuba a Dala Inland Dry Port Limited, da kuma dawo da kudin da ake zargin an karkatar.

Google search engine

Wadanda ake tuhuma sun hada da Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ‘ya’yansa Umar da Muhammad, tsohon mai ba shi shawara Abubakar Sahabo Bawuro, tsohon sakataren hukumar Nigerian Shippers Council Hassan Bello, lauya Adamu Aliyu Sanda, da kamfanin Dala Inland Dry Port Limited.

A cewar takardar tuhumar, ana zargin wadanda ake tuhumar da laifuka goma da suka hada da hada baki wajen karkatar da kudaden al’umma, cin amana da kuma sabawa doka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Manufofin tattalin arzikin Tinubu sun taimaka wajen samun dumbin arziki a Nijeriya – Hope Uzodimma

Gwamnan jihar Imo, Hope Uzodimma, ya ce manufofin tattalin arziƙin da shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bijiro dasu sun taimaka wajen farfaɗo da tattalin arziƙin...

Jami’ar kimiyya da fasaha ta Aliko Dangote da ke Wudil a Kano, ta kori dalibai 34 bayan an same su da laifin satar...

Jami’ar kimiyya da fasaha ta Aliko Dangote da ke Wudil a Kano, ta kori dalibai 34 bayan an same su da laifin satar amsa a...

Mafi Shahara