DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Kano ta yi karar Ganduje da ‘ya’yansa bisa zargin almundahanar Naira biliyan 4.49

-

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, da ‘ya’yansa biyu da wasu mutum shida kotu bisa zargin yin almundahanar kudi naira biliyan 4.49.

Gidan talabijin na Channels ya rawaito cewa an shigar da karar ne a babbar kotun jihar Kano a ranar 13 ga Oktoba, 2025, inda gwamnati ke neman a maido da kashi 20 cikin 100 na kudaden da aka zuba a Dala Inland Dry Port Limited, da kuma dawo da kudin da ake zargin an karkatar.

Google search engine

Wadanda ake tuhuma sun hada da Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ‘ya’yansa Umar da Muhammad, tsohon mai ba shi shawara Abubakar Sahabo Bawuro, tsohon sakataren hukumar Nigerian Shippers Council Hassan Bello, lauya Adamu Aliyu Sanda, da kamfanin Dala Inland Dry Port Limited.

A cewar takardar tuhumar, ana zargin wadanda ake tuhumar da laifuka goma da suka hada da hada baki wajen karkatar da kudaden al’umma, cin amana da kuma sabawa doka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara