DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dantawaye ya zama sabon kwamishinan ‘yan sandan Abuja

-

Rundunar ‘yan sanda ta babban birnin tarayya Abuja, ta sanar da fara aikin Dantawaye Miller a matsayin kwamishina na 34 da zai jagoranci rundunar a Abuja.

A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Josephine Adeh, ta fitar a Juma’ar nan, ta ce Miller ya karɓi ragamar ofishin daga tsohon kwamishina Ajao Adewale, wanda ya samu sabon mukami.

Google search engine

A cewar sanarwar, sabon kwamishinan ya yi alkawarin yin aiki tukuru tare da haɗin kai tsakanin rundunar da al’umma domin tabbatar da zaman lafiya a birnin tarayya Abuja.

Rundunar ta kuma roƙi jama’a su ci gaba da ba ‘yan sanda hadin kai wajen yakar muggan laifuka da tabbatar da tsaro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara