DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dantawaye ya zama sabon kwamishinan ‘yan sandan Abuja

-

Rundunar ‘yan sanda ta babban birnin tarayya Abuja, ta sanar da fara aikin Dantawaye Miller a matsayin kwamishina na 34 da zai jagoranci rundunar a Abuja.

A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Josephine Adeh, ta fitar a Juma’ar nan, ta ce Miller ya karɓi ragamar ofishin daga tsohon kwamishina Ajao Adewale, wanda ya samu sabon mukami.

Google search engine

A cewar sanarwar, sabon kwamishinan ya yi alkawarin yin aiki tukuru tare da haɗin kai tsakanin rundunar da al’umma domin tabbatar da zaman lafiya a birnin tarayya Abuja.

Rundunar ta kuma roƙi jama’a su ci gaba da ba ‘yan sanda hadin kai wajen yakar muggan laifuka da tabbatar da tsaro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Manufofin tattalin arzikin Tinubu sun taimaka wajen samun dumbin arziki a Nijeriya – Hope Uzodimma

Gwamnan jihar Imo, Hope Uzodimma, ya ce manufofin tattalin arziƙin da shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bijiro dasu sun taimaka wajen farfaɗo da tattalin arziƙin...

Jami’ar kimiyya da fasaha ta Aliko Dangote da ke Wudil a Kano, ta kori dalibai 34 bayan an same su da laifin satar...

Jami’ar kimiyya da fasaha ta Aliko Dangote da ke Wudil a Kano, ta kori dalibai 34 bayan an same su da laifin satar amsa a...

Mafi Shahara