DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An gudanar da addu’o’in neman tsari daga hare-haren ‘yan bindiga a jihar Neja

-

Mazauna yankin jihar Neja ta Arewa sun gudanar da addu’o’i na musamman a filin Idi da ke Kontagora, hedkwatar karamar hukumar Kontagora, domin neman taimakon Allah kan hare-haren ’yan bindiga da ke addabar al’ummomin karkara a yankin.

Rahotanni sun bayyana cewa, yankuna kamar Magama, Mariga, Rijau, Borgu, Kontagora da Mashegu sun fuskanci hare-hare a makonnin baya-bayan nan, lamarin da ya tilasta wa mata da yara da dama barin gidajensu.

Google search engine

Wani daga cikin ‘yan gudun hijirar da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa jaridar Daily Trust cewa, daruruwan mutane daga yankunan da ke fama da matsalar tsaro sun halarci taron addu’ar, inda suka roƙi Allah ya kawo musu saukin hare-haren ‘yan bindigar da masu basu bayanai da ma waɗanda ke tallafa musu.

Wasu mazauna yankin sun koka da cewa, sun tsere daga gidajensu yayin da ’yan bindiga suka kai farmaki a ƙauyukan nasu inda wasu suka kwana a kan duwatsu, wasu kuma suka koma Kontagora don tsira da rayukansu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan siyasa a Nijeriya sun fi maida hanakali kan siyasa maimakon magance matsalolin al’umma – Sarkin Onitsha

Sarkin Onitsha, Igwe Nnaemeka Achebe, ya caccaki ‘yan siyasa bisa mayar da hankali kan siyasa maimakon gudanar da mulki yadda ya kamata tun kafin zaben...

Wike ya musanta jita-jitar tsayawarsa takarar shugabancin Nijeriya a zaben 2027, ya jaddada goyon bayansa ga Tinubu har zuwa 2031

Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya karyata rahotannin da ke cewa wasu jiga-jigan jam’iyyar PDP na matsa masa lamba domin ya tsaya takarar shugaban ƙasa a...

Mafi Shahara