DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Barayin daji sun kai sabon samame a wani kauyen karamar hukumar Kusada, jihar Katsina

-

Bayanai daga kauyen Tittike da ke mazabar Boko a karamar hukumar hukumar Kusada jihar Katsina na cewa barayin daji sun kai hari inda suka yi sanadiyyar asarar dumbin dukiyoyi.

A cikin wani sakon jajanta wa da dan majalisar wakilai daga kananan hukumomin Kankia/Kusada/Ingawa Abubakar Yahaya Kusada ya wallafa a shafinsa na Facebook, ya jajanta bisa wannan abin da ya kira ibtila’i.

Google search engine

Ya ce “Cikin alhini da kaduwa nake mika sakon jajantawa ga Al’ummar TITTIKE dake Boko ward, a karamar hukumar kusada bisa ibtila’in shigowar yan bindiga”.

“Al’ummarmu sun yi asarar dukiyoyinsu da kuma daukar daya daga cikin matasanmu da muke alfahari da shi wato Malam Kamilu Abdurrahman Tela. Ina jajanta mana bisa wannan ibtila’i da ya shafi Al’ummarmu”.

Ba za mu gajiya ba wajen shige da fice da muke yi don ganin wannan matsala ta zama tarihi, Allah ya ba mu mafita Amin”.

Karamar hukumar Kusada dai na iyaka da Kankia, inda ake samun matsalar tsaro jefi-jefi a jihar Katsina

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan siyasa a Nijeriya sun fi maida hanakali kan siyasa maimakon magance matsalolin al’umma – Sarkin Onitsha

Sarkin Onitsha, Igwe Nnaemeka Achebe, ya caccaki ‘yan siyasa bisa mayar da hankali kan siyasa maimakon gudanar da mulki yadda ya kamata tun kafin zaben...

Wike ya musanta jita-jitar tsayawarsa takarar shugabancin Nijeriya a zaben 2027, ya jaddada goyon bayansa ga Tinubu har zuwa 2031

Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya karyata rahotannin da ke cewa wasu jiga-jigan jam’iyyar PDP na matsa masa lamba domin ya tsaya takarar shugaban ƙasa a...

Mafi Shahara