DCL Hausa Radio
Kaitsaye

APC ba ta da juriyar ra’ayoyin jam’iyyun adawa – Rauf Aregbesola

-

Sakataren jam’iyyar ADC Ogbeni Rauf Aregbesola, ya zargi jam’iyyar APC mai mulki da rashin jurewa ra’ayoyin ‘yan adawa da kuma amfani da ƙarfin gwamnati wajen murkushe su .

Aregbesola ya bayyana hakan ne yayin kaddamar da ofishin ADC a garin Ilori jihar Kwara, inda ya ce gwamnatin APC ta gaza saboda son kai da rashin ƙwarewa, abin da ya jefa ƙasar cikin yunwa, rashin tsaro da durkushewar ayyukan gwamnati.

Google search engine

Ya kara da cewa yanzu haka yunwa ta mamaye ƙasa, ta mayar da mulki hanyar tara wa kai dukiya da tsoratar da ‘yan adawa.

Aregbesija ya ce ‘yan Nijeriya na fama da wahala saboda gazawar shugabanni a karkashin APC.

Hakazalika, jaridar Punch ta ruwaito Aregbesola ya ce, jam’iyyar ADC ita ce jam’iyyar da ke da muradin gaskiya da hidima ga jama’a, sannan abin dogaro ga ‘yan Nijeriya gabanin zaben 2027.

A cewarsa, ƙiyayyar ‘yan Nijeriya ga APC ta bayyana, kuma ADC ce za ta amfana da hakan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara