DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu babbar kyauta ne daga Allah domin gyaran Nijeriya – Yahaya Bello

-

Tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello ya bayyana shugaban Nijeriya Bola Tinubu a matsayin babbar kyauta da Allah ya ba Nijeriya domin gyaran kasar.

Yahaya Bello ya faɗi haka ne a yayin wani gangamin nuna goyon baya ga shugaba Tinubu da gwamnan Kogi Usman Ododo da aka gudanar a ranar Asabar, wanda aka watsa kai tsaye a gidan talabijin na TVC.

Google search engine

A cewarsa, gyaran ƙasa yana ɗaukar lokaci saboda matsalolin da aka gada, yana kuma roƙon ‘yan Nijeriya su ba shugaba Tinubu goyon baya domin cika alkawurran da ya dauka

Tsohon gwamnan ya jaddada cewa Tinubu kyauta ne daga Allah ga yan Nijeriya domin gyaranta, ya kuma yaba wa gwamnatin Tinubu bisa sauye-sauyen da ta aiwatar, ciki har da cire tallafin mai, samar da rancen kudi na karatu ga ɗalibai, da sauran su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Nijeriya ta ce cin jarabawar lissafi “Mathematics” wajibi ne ga daliban Sakandare kafin kammalawa

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa lallai dukkan ɗalibai masu rubuta jarabawar kammala sakandare su cigaba da rubuta lissafi tare da harshen Turanci a matsayin wajibi. Mai...

Kaso 95 cikin 100 na jihar Kaduna ‘yan APC ne – Uba Sani

Jam’iyyar APC a jihar Kaduna ta karɓi sabbin mambobi, ciki har da ’yan majalisar wakilai guda biyar da kuma ’yan majalisar dokokin jihar Kaduna huɗu...

Mafi Shahara